Ayatullah Muhammad Javad Fazel Lankarani a cikin taron dare na sansanin al'adu na Jami'ar Tulu' Mehr a dandalin Risalat na Qom, yayin da yake karanta ayar:
«إِنَّ الَّذِینَ قَالُوا رَبُّنَا اللَّهُ ثُمَّ اسْتَقَامُوا تَتَنَزَّلُ عَلَیْهِمُ الْمَلَائِکَةُ»
"Lalle ne waɗanda suka ce: Ubangijinmu Allah ne, sa'an nan suka tsayu, mala'iku suna sauka a garesu," ya bayyana tsayin daka na shekaru 47 na al'ummar Iran a matsayin babban misali na saukar mala'iku, kuma ya ce: A yau ana ganin tasirin hakan ga mutanen da suka ji labarin harin makiya, amma maimakon su gudu zuwa wuraren fakewa, sai su ka tsaya a kan rufin gidaje suna kallo, ba su da wani tsoro ko fargaba.
.......................
Your Comment